Home Labarai Matasa sun fasa wurin ajiyar shinkafa a jihar Kano

Matasa sun fasa wurin ajiyar shinkafa a jihar Kano

Rahotanni daga unguwar Gandun albasa da ke karamar hukumar birni a jihar kano, na tabbatar da cewa wasu matasa sun farwa wata makaranta mai suna Wada Sagagi, inda suka kwashi shinkafa mai rubutun gwamnatin tarayya a jikin buhunta.

Wasu mazauna unguwar sun ce, matasan sun shiga gidan ne da talatainin daddare, domin kwasar shinkafar da ake zargin wadda gwamnatin tarayya ta aiko ne domin rabawa mabukata a jihar.

Makarantar dai, na zaune ne a tsohon gidan shugaban ma’aikata na fadar gwamnatin Kano, Alh Shehu Wada Sagagi.

sai dai kawo yanzu shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano Shehu Wada Sagagi da ake zargin na da alaka da kayan, bai ce komai ba.

Amma shugaban makarantar Islamiyyar ta Wada Sagagi ya tabbatar da faruwar shigar matasan cikin makarantar tare da kwasar buhunhunan shinkafar.

Idan za a iya tunawa makwani biyu da suka gabata, gwamnatin tarayya ta ce ta turawa gwamnonin jihohin Kasar tirela 20 ta Shinkafa zuwa kowacce jiha domin rabawa talakawa don magance matsalolin matsin rayuwa da ake ciki a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp