Home Labarai Mun Kama ‘yanƙasar Poland bakwai a Kano kan ɗaga tutar Rasha a...

Mun Kama ‘yanƙasar Poland bakwai a Kano kan ɗaga tutar Rasha a zanga-zanga – DSS

Jami’an tsaro a Najeriya sun kama ‘yan ƙasar Poland bakwai bisa zargin ɗaga tutocin Rasha yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa a jihar Kano da ke arewacin ƙasar.

Kakakin rundunar tsaron farin kaya, Peter Afunanya, ya faɗa yayin taron manema labarai a yau Laraba cewa sun kama su ne lokacin da jami’ansu ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro.

Sai dai bai yi ƙarin bayani ba game da ko su wane ne, amma ba farautar ‘yan ƙasar ta Poland a Najeriya suke yi ba.

Kamfanin labarai na Reuters ya ruwaito jakadan Poland a Najeriya, Stanislaw Gulinski, yana tabbatar da kamen yayin ganawar da jakadu suka yi da gwamnatin Najeriya ranar Laraba a Abuja.

“An kama su kwana biyu da suka wuce a Kano, abu na ƙarshe da na ji shi ne ana shirin kawo su Abuja a jirgi,” in ji shi.

Sai dai ya ƙi yin ƙarin bayani lokacin da Reuters ya tuntuɓe shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp