Home Labarai Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake yin roƙo ga ƴan ƙasar su ƙara yi wa gwamnatinsa haƙuri inda ya ce sauƙi na nan tafe.

Shugaban ya sake yin jawabi ne ga ƴan Najeriya a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba bayan jawabin farko da ya yi a ranar Lahadi saboda zanga-zangar tsadar rayuwa da kuma adawa da matakansa na tattalin arziki.

A cikin jawabin shugaban, ya nanata cewa yana sane da ƙuncin rayuwa da ƴan Najeriya suka shiga sakamakon janye tallafin fetur.

Ƴan Najeriya da dama ne suka fantsama a titunan biranen ƙasar domin zanga-zangar tsadar rayuwa, inda wasunsu da dama ke kira ga shugaban ya dawo da tallafin da ya cire na man fetur da suka ce ya jefa su cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa.

Amma a sabon jawabinsa, shugaban ya ce yana sane da wahalar da ƴan Najeriya ke ciki tare da nanata cewa wahala ce ta ɗan ƙaramin lokaci.

“Wannan lokacin zai iya zama mai wahala a gare mu amma ina son mu yi hangen gaba a cikin wahalar da muke ciki da kuma la’akari da babbar manufar. Mun yi tsare-tsare masu kyau kuma na san za su yi aiki,” in ji Shugaba Tinubu.

Sai dai shugaban ya amince cewa tsare-tsaren da gwamnatinsa ke ɗauka sun ƙara wa ƴan Najeriya raɗaɗin janye tallafin fetur.

Amma ya ce ya yi imanin matakan gwamnatinsa ke ɗauka za su magance matsalolin tattalin arzikin da Najeriya ke ciki.

“Ina roƙon ku, ku yi haƙuri tare da imanin cewa za mu iya da kuma damuwar da muke nunawa kan buƙatunku. Za mu fita daga cikin wannan ƙangin, kuma saboda matakan da muke ɗauka Najeriya za ta samu ci gaba da kuma more makomarta,” a cewar shugaba Tinubu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp