Home Labarai Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Ina sane da halin kuncin da kuke ciki – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake yin roƙo ga ƴan ƙasar su ƙara yi wa gwamnatinsa haƙuri inda ya ce sauƙi na nan tafe.

Shugaban ya sake yin jawabi ne ga ƴan Najeriya a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba bayan jawabin farko da ya yi a ranar Lahadi saboda zanga-zangar tsadar rayuwa da kuma adawa da matakansa na tattalin arziki.

A cikin jawabin shugaban, ya nanata cewa yana sane da ƙuncin rayuwa da ƴan Najeriya suka shiga sakamakon janye tallafin fetur.

Ƴan Najeriya da dama ne suka fantsama a titunan biranen ƙasar domin zanga-zangar tsadar rayuwa, inda wasunsu da dama ke kira ga shugaban ya dawo da tallafin da ya cire na man fetur da suka ce ya jefa su cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa.

Amma a sabon jawabinsa, shugaban ya ce yana sane da wahalar da ƴan Najeriya ke ciki tare da nanata cewa wahala ce ta ɗan ƙaramin lokaci.

“Wannan lokacin zai iya zama mai wahala a gare mu amma ina son mu yi hangen gaba a cikin wahalar da muke ciki da kuma la’akari da babbar manufar. Mun yi tsare-tsare masu kyau kuma na san za su yi aiki,” in ji Shugaba Tinubu.

Sai dai shugaban ya amince cewa tsare-tsaren da gwamnatinsa ke ɗauka sun ƙara wa ƴan Najeriya raɗaɗin janye tallafin fetur.

Amma ya ce ya yi imanin matakan gwamnatinsa ke ɗauka za su magance matsalolin tattalin arzikin da Najeriya ke ciki.

“Ina roƙon ku, ku yi haƙuri tare da imanin cewa za mu iya da kuma damuwar da muke nunawa kan buƙatunku. Za mu fita daga cikin wannan ƙangin, kuma saboda matakan da muke ɗauka Najeriya za ta samu ci gaba da kuma more makomarta,” a cewar shugaba Tinubu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp