Home Labarai Mayakan boko haram 50 sun mika wuya ga Sojoji a jihar Borno

Mayakan boko haram 50 sun mika wuya ga Sojoji a jihar Borno

Nigerian Army

Dakarun sojojin kasan Nijeriya sun sami nasarar kama kwamandan kungiyar Boko, mai kai musu kaya da kuma wadanda suke hada baki, gami da mayakan kungiyar da suka mika wuya da iyalansu.

Haka kuma dakarun rundunar sun sami nasarar kwato wadanda mayakan kungiyar suka yi garkuwa da su a mabambanta maboyar su, haka kuma dakarun sun sami nasarar kwato wasu kayyaki da bata gari suka sace a yayin gudanar da zanga-zangar luma a kasar.

Rundunar sojojin tace a ranar 4 ga watan Agusta, 2024 bisa aiki da wasu bayanan sirri dake yi ta sami nasarar kama wasu kwamandojin mayakan kungiyar boko haram a jihar Borno, wadanda ke yunkurin kutsawa sansanin ‘yan gudun hijira dake Damasak a karamar hukumar Mobbar.

Wadanda ake zargin da suka hadar da Bana Yamode da babagana Usman, wanda suka yi ikirarin sun je sansanin ne domin ziyartar iyalen su, wadanda tun da fari dama su sukayi jagoranci kai hari a yankin.

Haka kuma dakarun sun sami nasara kama wadanda ake zargi da safarar kayayyaki guda biyu Mallam Mustapha Isma’il mai shekaru 49 da kuma Abdulmudalibi Haruna mai shekaru 30, tare da ceto wasu mutum biyu a yayin sumamen.

Haka kuma mayakan boko haram 50 da iyalansu sun mika wuya ga rundunar a kananan hukumomin Bama, Gwoza da Dikwa, wannan dai na zuwa ne bisa yunkurin dakarun sojojin na kakkabe mayakan na boko haram.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp