Al’ummar Nijeriya na shakku kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal

Kungiyar dilalan man fetur ta kasar nan tace nan da makwanni uku masu zuwa matatar mai ta fatakwal zata fara aiki yadda ya kamata, domin cimma umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar na watan Agusta.

Haka kuma kungiyar tace matatar zata ke fitar da mai lita miliyan 10 zuwa miliyan 12 ga ‘yan kasuwa.

Contirolan ayyukan na kungiyar Zarma Mustapha ne ya bayyana hakan yayyin da yake ganawa da kafar yada labarai ta NTA, inda yace matatar man zata habaka samar da man a kasar nana daga lita miliyan 11 zuwa 15 a ko wacce, gami da samar da wadataccen makamashi.

Haka kuma matatar zata yi aiki ne bisa zaman kanta, kuma zata sayar da man ne bisa farashin kasuwa ba tare da gwamnatin tarayya tayi mata katsandan ba.

Ko da yace bayan bayyana wannan kudiri Al’ummar kasar nan sun bayyana cewa sun gaji da gafara sa basu ga kaho ba, duba da yadda aka yi ta yi musu alkawurra amma babu guda daya da aka cika akan matatun na kasar nan.

Idan dai za’a iya tunawa mahukunta a kasar nan sun bayyanawa al’umma cewa matata zata fara aiki watan disambar 2023, idan aka hada da wannan alkawari gwamantin tarayyar kasar nan tayi alkawarin sau hudu kenan tun bayan darewarta kan karagar mulki.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 36 minutes 17 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 17 minutes 42 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com