Home Labarai Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar...

Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake kira ga ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso da su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban, wanda kuma shine shugaban ƙungiyar ta ECOWAS a lokaci guda na jadadda wannan roƙo ne lokacin da yake ganawa da manyan hafsohin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS a Abuja.

Ya ce babbar buƙatar ƙungiyar a yanzu shine dawo da ƙasashen cikin ECOWAS, la’akari da muhimmanci da suke da shi, musamman ta fannin tsaro.

A cewar sa, shugabancin Najeriya da kuma na ECOWAS a lokaci guda ya sanya jagorancin ƙungiyar ya kasance mai matuƙar tsauri a gareshi, don haka zai yi duk mai yiwuwa don ganin sun dawo cikin ƙungiyar ba tare da wani tashin hankali ba.

Shugaban na Najeriya ya gargadi ƙasashen kan cewa dagewar da suka yi na ƙin komawa ECOWAS ba zai haifar musu da komai ba illa koma baya, la’akari da cewa duk abinda za’a yi shi a ƙungiyance yafi armashi da kuma tasiri.

Daga nan kuma sai Tinubu ya yabawa shugabannin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS kan irin kwarewar aiki da suka nuna ta yadda har yanzu yaƙi bai barke tsakanin su da ƙasashen da suka yi iƙirarin ficewa daga ƙungiyar ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp