Home Labarai Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar...

Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake kira ga ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso da su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban, wanda kuma shine shugaban ƙungiyar ta ECOWAS a lokaci guda na jadadda wannan roƙo ne lokacin da yake ganawa da manyan hafsohin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS a Abuja.

Ya ce babbar buƙatar ƙungiyar a yanzu shine dawo da ƙasashen cikin ECOWAS, la’akari da muhimmanci da suke da shi, musamman ta fannin tsaro.

A cewar sa, shugabancin Najeriya da kuma na ECOWAS a lokaci guda ya sanya jagorancin ƙungiyar ya kasance mai matuƙar tsauri a gareshi, don haka zai yi duk mai yiwuwa don ganin sun dawo cikin ƙungiyar ba tare da wani tashin hankali ba.

Shugaban na Najeriya ya gargadi ƙasashen kan cewa dagewar da suka yi na ƙin komawa ECOWAS ba zai haifar musu da komai ba illa koma baya, la’akari da cewa duk abinda za’a yi shi a ƙungiyance yafi armashi da kuma tasiri.

Daga nan kuma sai Tinubu ya yabawa shugabannin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS kan irin kwarewar aiki da suka nuna ta yadda har yanzu yaƙi bai barke tsakanin su da ƙasashen da suka yi iƙirarin ficewa daga ƙungiyar ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp