Home Labarai Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar...

Tinubu- Bukatar mu Nijar, Mali da Burkina Faso su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake kira ga ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso da su koma cikin ƙungiyar ECOWAS.

Shugaban, wanda kuma shine shugaban ƙungiyar ta ECOWAS a lokaci guda na jadadda wannan roƙo ne lokacin da yake ganawa da manyan hafsohin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS a Abuja.

Ya ce babbar buƙatar ƙungiyar a yanzu shine dawo da ƙasashen cikin ECOWAS, la’akari da muhimmanci da suke da shi, musamman ta fannin tsaro.

A cewar sa, shugabancin Najeriya da kuma na ECOWAS a lokaci guda ya sanya jagorancin ƙungiyar ya kasance mai matuƙar tsauri a gareshi, don haka zai yi duk mai yiwuwa don ganin sun dawo cikin ƙungiyar ba tare da wani tashin hankali ba.

Shugaban na Najeriya ya gargadi ƙasashen kan cewa dagewar da suka yi na ƙin komawa ECOWAS ba zai haifar musu da komai ba illa koma baya, la’akari da cewa duk abinda za’a yi shi a ƙungiyance yafi armashi da kuma tasiri.

Daga nan kuma sai Tinubu ya yabawa shugabannin tsaron ƙasashe mambobin ECOWAS kan irin kwarewar aiki da suka nuna ta yadda har yanzu yaƙi bai barke tsakanin su da ƙasashen da suka yi iƙirarin ficewa daga ƙungiyar ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp