Home Labarai Al’ummar Nijeriya na shakku kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal

Al’ummar Nijeriya na shakku kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal

Kungiyar dilalan man fetur ta kasar nan tace nan da makwanni uku masu zuwa matatar mai ta fatakwal zata fara aiki yadda ya kamata, domin cimma umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar na watan Agusta.

Haka kuma kungiyar tace matatar zata ke fitar da mai lita miliyan 10 zuwa miliyan 12 ga ‘yan kasuwa.

Contirolan ayyukan na kungiyar Zarma Mustapha ne ya bayyana hakan yayyin da yake ganawa da kafar yada labarai ta NTA, inda yace matatar man zata habaka samar da man a kasar nana daga lita miliyan 11 zuwa 15 a ko wacce, gami da samar da wadataccen makamashi.

Haka kuma matatar zata yi aiki ne bisa zaman kanta, kuma zata sayar da man ne bisa farashin kasuwa ba tare da gwamnatin tarayya tayi mata katsandan ba.

Ko da yace bayan bayyana wannan kudiri Al’ummar kasar nan sun bayyana cewa sun gaji da gafara sa basu ga kaho ba, duba da yadda aka yi ta yi musu alkawurra amma babu guda daya da aka cika akan matatun na kasar nan.

Idan dai za’a iya tunawa mahukunta a kasar nan sun bayyanawa al’umma cewa matata zata fara aiki watan disambar 2023, idan aka hada da wannan alkawari gwamantin tarayyar kasar nan tayi alkawarin sau hudu kenan tun bayan darewarta kan karagar mulki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp