Tinubu zai kai ziyara Faransa

Fadar Shugaban Najeriya Bola Tinubu ta bayyana cewa shugaban zai yi tafiya zuwa ƙasar Faransa a yau Litinin.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Ba a fayyace makasudin ziyarar ba, amma ana sa ran Tinubu zai dawo Najeriya bayan wani dan lokaci kadan.

Ziyarar ta biyo bayan wata ziyarar da shugaban ƙasar ya kai a kasar Equatorial Guinea a baya-bayan nan, inda ya gana da shugaban ƙasar Teodoro Mbasogo, tare da sanya hannu kan yarjejeniyoyin da suka shafi man fetur da iskar gas, da kuma tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com