Home Labarai Ana tsare da masu zanga-zangar tsadar rayuwa fiye da 1000 a Najeriya

Ana tsare da masu zanga-zangar tsadar rayuwa fiye da 1000 a Najeriya

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta Amnesty International, ta bayyana cewa sama da masu zanga-zangar tsadar rayuwa 1,000 ne ke tsare a hannun hukumomin Najeriya sakamakon shiga zanga-zangar tsadar rayuwa ta baya-bayan nan.

Zanga-zangar wadda aka gudanar tsakanin ranakun 1 zuwa 10 ga watan Agusta ta rikiɗe zuwa tarzoma a wasu sassan ƙasar, inda aka samu rahotannin sace-sace da lalata kadarorin gwamnati a wasu jihohi.

Hukumomin tsaro a Najeriyar sun ce sun kama mutane da dama da ake zargi da hannu a yamutsin.

To sai dai a cewar kungiyar ta Amnesty International, da dama daga cikin mutanen da aka kama waɗanda ba su aikata laifi ba ne.

Malam Isa Sanusi, daraktan ƙungiyar a Najeriya, ya ce an kama mutane mutum 632 a Jihar Kano, yayin da kuma a Sokoto an kama mutane za su kai 109 sannan kuma a Jihar Borno an kama mutum sama da 100.

“A Bauchi ma an kama mutane sannan kuma mun samu labarin cewa Kaduna ma an kama mutane za su kai 70, a Katsina ma mutum 70 aka kama.” in ji daraktan.

“To, mutanen dai suna rarrabe ne a duka jihohi, har yanzu ba mu gama ƙididdigewa ba amma zuwa yanzu ƙididdigar da muka samu kan mutanen da aka kama sun fi 100,” kamar yadda darektan ya bayyana.

Daraktan ya kuma ce “a duk lokacin da aka yi irin wannan zanga-zangar, muna sane da cewa ana yin kame na kan mai-uwa-da-wabi sannan ana kama mutanen da suka yi laifi da waɗanda ba su yi laifi ba inda a ƙarshe waɗanda suka shiga zanga-zangar ba tare da aikata laifin komai ba, sai a nemi wani laifi a laƙa masu wanda ba su aikata ba.”

An dai ga yadda zanga-zangar ta haifar da yamutsi a jihohin Kano da Jigawa da Kaduna da Katsina.

Wannan ya sanya aka ƙaƙaba dokar hana fita ta ba dare ba rana a jihohi da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp