Home Labarai NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

Kamfanin mai na Nigeria NNPC ya ce ya damu matuka bisa yadda ake fuskantar karancin man fetur a wasu sassan Nigeria.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban jami’in sadarwa na kamfanin Olufemi Sonete ya fitar wadda aka raba manema labarai.

Ta cikin sanarwar NNPCL ya danganta matsalar da kalubalen aiki rarraba man fetur din a fadin kasar.

Haka kuma sanarwar tace NNPCL yana kira ga masu ababen hawa da su kara hakuri, yana aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki don shawo kan matsalar.

Al’ummar wasu sassan Nijeriya dai na fuskantar ƙarancin man fetur wanda hakan ya sanya ake sayar da man daga kan Naira 800 har yanzu Naira 950.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp