• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Cutar diphtheria ta kashe mutane 40 bayan sake ɓulla a Kano
  • General
  • Labarai

Cutar diphtheria ta kashe mutane 40 bayan sake ɓulla a Kano

By
Diphtheria, Kano
-
August 29, 2024
Arewa Award

Sabuwar annobar cutar mashaƙon diphtheria da ta ɓarke a jihar Kano ta arewacin Najeriya ta laƙume rayukan fiye da mutane 40 yayinda wasu gommai yanzu haka ke kwance a asibitoci don karɓar kulawa bayan harbuwa da cutar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito yadda wakilinta ya ganewa idonsa cikar asibitin kula da cutuka masu yaɗuwa na jihar Kano da ake kira IDH ko kuma ‘zana’ maƙil da waɗanda suka harbu da cutar.

Wani jami’in asibitin da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar mata da yawaitar mutuwar da ake gani kullu yaumin sanadiyyar cutar a cikin nasibitin na Zana ko kuma IDH.

Bayanai sun ce har zuwa tsakar ranar jiya anga dandazon marasa lafiyar da ke son ganin likita a asibitin na Zana sakamakon alamomin cutar ta mashaƙon diphtheria.

Read Also:

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

Rahotanni sun ce makwanni biyu kenan a jere ana ganin ƙaruwar masu fama da wannan cuta da kan riƙe maƙogwaro tare da haddasa zazzabi da kuma ƙuraje a baki ko ɗaɗewar harshe da sauyawar kalar ido.

Wasu majiyoyi sun ce rashin kayakin aiki dama ƙwararrun likitocin da ke duba wannan cuta a sassan jihar shi ne ya haddasa cunkoson jama’a a asibitin wanda ke tsakar birnin Kano.

Tuni dai masu ruwa da tsaki suka ɗaura ɗamarar fara aikin wayar da kan jama’a game da alamomin cutar da kuma yadda za a baiwa kai kariya daga harbuwa da ita, lura da kasancewar cutar ta diphtheria a sahun cutukan da wani kan gogawa wani.

Alƙaluma sun nuna cewa wannan cuta ta fi illa ga ƙananan yara ta yadda ta ke farowa kamar mura gabanin tsananta tare da haddasa asarar rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleShugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci
Next articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Diphtheria, Kano

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna

Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi

An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro

Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

karo na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewa

Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara

Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano – Gwamnati

JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Gwamnan Kano zai koma Jam’iyyar APC

Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Recent Posts

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar
  • Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro
  • Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1687 days 19 hours 9 minutes 30 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1669 days 20 hours 50 minutes 55 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a KadunaBa a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya - Sanata NingiAn ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin NijarTurkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar TsaroNajeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasarkaro na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewaMatatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban baraAna tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano - GwamnatiJOHESU - Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma'aikatan asibitiGwamnan Kano zai koma Jam'iyyar APCGwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci
X whatsapp