Home General Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, bisa rakiyar ƴan ƙungiyar ƙwadago da Femi Falana, lauyoyi da suka haɗ da Femi Falana lauya mai rajin kare hakkin ɗanadam a Najeriya da Deji Adeyanju, ya gana da ƴansanda a hedikwatarsu da ke babban birnin tarayya domin amsa gayyatar suka yi masa.

Rundunar ‘yan sandan dai ta gayyaci shugaban NLC ɗin ne bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta’addanci, wanda shugaban da ƙungiyar suka musanta.

Tun da karfe takwas na safe ne shugabannin NLC ɗin suka fara hallara a hedikwatarsu, inda suka gudanar da gangamin nuna hadin kai da goyon baya ga Ajaero.

Bidiyon da aka wallafa a shafin sada zumuntar NLC na X sun nuna wasu shugabannin kwadagon suna jawabi ga ma’aikatan da suka taru, wadanda suka tsaya kyam a bayan Shugaban nasu.

Kawo yanzu dai babu cikakken bayani na haƙiƙanin abin da ya faru a yayin ganawar.

Tun da farko dai ‘yan sandan sun gayyaci Ajaero a makon da ya gabata, bisa zargin bayar da kudade ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan sada zumunta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp