Home General Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, bisa rakiyar ƴan ƙungiyar ƙwadago da Femi Falana, lauyoyi da suka haɗ da Femi Falana lauya mai rajin kare hakkin ɗanadam a Najeriya da Deji Adeyanju, ya gana da ƴansanda a hedikwatarsu da ke babban birnin tarayya domin amsa gayyatar suka yi masa.

Rundunar ‘yan sandan dai ta gayyaci shugaban NLC ɗin ne bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta’addanci, wanda shugaban da ƙungiyar suka musanta.

Tun da karfe takwas na safe ne shugabannin NLC ɗin suka fara hallara a hedikwatarsu, inda suka gudanar da gangamin nuna hadin kai da goyon baya ga Ajaero.

Bidiyon da aka wallafa a shafin sada zumuntar NLC na X sun nuna wasu shugabannin kwadagon suna jawabi ga ma’aikatan da suka taru, wadanda suka tsaya kyam a bayan Shugaban nasu.

Kawo yanzu dai babu cikakken bayani na haƙiƙanin abin da ya faru a yayin ganawar.

Tun da farko dai ‘yan sandan sun gayyaci Ajaero a makon da ya gabata, bisa zargin bayar da kudade ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan sada zumunta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp