Home General Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna tace sojoji sun hallaka ‘yan bindiga takwas a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar alhamis.

Yace sakamakon wani sumame da dakarun sojin suka kai yankin Kamfanin Doka, ne suka yi arba da ‘yan bindigar a yankin, nan suka hau musayar wuta ne sojojin suka sami nasarar hallaka bakwai daga cikin su.

“Ya yin da sojojin ke bincike a yankin sun sami nasarar bankado bindiga kirar AK47 guda uku, gami da gidan saka alburushi guda takwas, wanda suka kunshi hudu babu komai a cikin su sai kuma hudu dauke da alburusai 120 masu tsahon 7.62mm.” a cewar sa.

Aruwan ya kara da cewa sun kuma sami nasarar kwato kayayyakin da suka hadar da babu 6, wayoyin hannun uku, sai kuma radio kirar Baofeng, da kuma kayan fararen hula.

Haka kuma ya kara da cewa yayin da sojojin ke karkare atisayen sun sake yin wata arangamar da ‘yan ta’addan a yankin Gayam.

“Sojojin sun sami nasarar hallaka daya daga cikin su yayin da ake zargin sauran sun gudu da raunikan harbi a jikin su.” Kamar yadda ya bayyan.

Aruwana ya kara da cewa Gwamnan jihar Uba Sani ya yaba da kokarin dakarun bisa wannan nasara da suka samu a yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi sassan jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp