Home General Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna tace sojoji sun hallaka ‘yan bindiga takwas a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar alhamis.

Yace sakamakon wani sumame da dakarun sojin suka kai yankin Kamfanin Doka, ne suka yi arba da ‘yan bindigar a yankin, nan suka hau musayar wuta ne sojojin suka sami nasarar hallaka bakwai daga cikin su.

“Ya yin da sojojin ke bincike a yankin sun sami nasarar bankado bindiga kirar AK47 guda uku, gami da gidan saka alburushi guda takwas, wanda suka kunshi hudu babu komai a cikin su sai kuma hudu dauke da alburusai 120 masu tsahon 7.62mm.” a cewar sa.

Aruwan ya kara da cewa sun kuma sami nasarar kwato kayayyakin da suka hadar da babu 6, wayoyin hannun uku, sai kuma radio kirar Baofeng, da kuma kayan fararen hula.

Haka kuma ya kara da cewa yayin da sojojin ke karkare atisayen sun sake yin wata arangamar da ‘yan ta’addan a yankin Gayam.

“Sojojin sun sami nasarar hallaka daya daga cikin su yayin da ake zargin sauran sun gudu da raunikan harbi a jikin su.” Kamar yadda ya bayyan.

Aruwana ya kara da cewa Gwamnan jihar Uba Sani ya yaba da kokarin dakarun bisa wannan nasara da suka samu a yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi sassan jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp