Shugaban kungiyar dake rajin kare hakkin Dan Adam da wayar da kai (CHRICED) Dakta Ibrahim M Zikirullahi ya bayyana cewa, Jahar Kano na kokari wajen tabbatar da an samu Cigaba mai dorewa a fannin lafiya ta bangare Samar da doka akan rage mace mace mata Masu juna biyu da kananan yara tun lokacin Tsohon Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso a shekarar 2001.
Dakta Ibrahim ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da manema labarai da kuma kungiyoyi Masu zaman kan su kan Samar da hanyoyin magance matsalar yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara ta Samar da dabaru don zantar da dokar haihuwa kyauta.
Read Also:
Kididiga na nuna cewa, jihar Kano na Cigaba da zama a sahu farko wajen samun yawan Mace -mace mata Masu juna biyu da kananan yara a kasar, Wanda haka ya zama barazana ga fannin lafiya a kasa.
Dakta Ibrahim ya Kara da cewa, rashin zartar da dokar haihuwa kyauta a asibitocin mu na Kara yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara.
Hakazalika, zartar da dokar zai Kara bawa kananon asibitocin da ke a matakin farko Samar Samu kulawa tare da horar da likitoci da kuma Kara inganci aikin su .
Tabbas Gwamnoni da ake yi a Kano sunyi kokari wajen Samar da Dokar Wanda har yanzu wasu jahohin na matakin farko,sai dai zartar da dokar a jahar na zama tsaiko idan ka ga yadda kididiga ke nuna wa tun bayan kaddamar da dokar a watan mayu shekarar 2023.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1187 days 18 hours 1 minute 32 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 42 minutes 57 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com