Home General Jihar Kano na Sahun gaba wajen Mace-Macen mata masu Juna Biyu

Jihar Kano na Sahun gaba wajen Mace-Macen mata masu Juna Biyu

Shugaban kungiyar dake rajin kare hakkin Dan Adam da wayar da kai (CHRICED) Dakta Ibrahim M Zikirullahi ya bayyana cewa, Jahar Kano na kokari wajen tabbatar da an samu Cigaba mai dorewa a fannin lafiya ta bangare Samar da doka akan rage mace mace mata Masu juna biyu da kananan yara tun lokacin Tsohon Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso a shekarar 2001.

Dakta Ibrahim ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da manema labarai da kuma kungiyoyi Masu zaman kan su kan Samar da hanyoyin magance matsalar yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara ta Samar da dabaru don zantar da dokar haihuwa kyauta.

Kididiga na nuna cewa, jihar Kano na Cigaba da zama a sahu farko wajen samun yawan Mace -mace mata Masu juna biyu da kananan yara a kasar, Wanda haka ya zama barazana ga fannin lafiya a kasa.

Dakta Ibrahim ya Kara da cewa, rashin zartar da dokar haihuwa kyauta a asibitocin mu na Kara yawan mace-mace mata Masu juna biyu da kananan yara.

Hakazalika, zartar da dokar zai Kara bawa kananon asibitocin da ke a matakin farko Samar Samu kulawa tare da horar da likitoci da kuma Kara inganci aikin su .

Tabbas Gwamnoni da ake yi a Kano sunyi kokari wajen Samar da Dokar Wanda har yanzu wasu jahohin na matakin farko,sai dai zartar da dokar a jahar na zama tsaiko idan ka ga yadda kididiga ke nuna wa tun bayan kaddamar da dokar a watan mayu shekarar 2023.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp