Home General Gwamnatin kano ta bayyana ranar komawa makarantu a jihar

Gwamnatin kano ta bayyana ranar komawa makarantu a jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta saka ranar 16 ga watan Satumba domin komawa makarantar Firamare da Sakandire na zangon farko na shekarar 2024/2025 ga dukkan makarantun kwana da na firamare masu zaman kansu dake jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu aka raba ta ga manema labarai a jihar, wadda ta ce ta iyaye da wakilansu su lura da sabuwar ranar da za su ci gaba da aiki domin tabbatar da bin doka.

sanarwar ta ce Makarantun kwana a fadin jihar za su koma ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024.

Idan dai ba a manta ba, kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya sanar a ranar Asabar 7 ga watan Satumba, dage ranar da za a koma makaranta.

Sanarwar ta sake jaddada kudurin gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusif na ganin kowane yaro ya samu ilimi mai inganci.

“Gwamnati na daukar matakai masu kyau wajen samar da ingantaccen yanayin koyo da zai zaburarwa da karfafawa dalibanmu kwarin gwiwa a fannin ilimi,” in ji sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp