Home General Hadaddiyar Daular larabawa ta sake korar ‘yan Nijeriya

Hadaddiyar Daular larabawa ta sake korar ‘yan Nijeriya

Mahukuntan Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun tiso keyar ƴan Najeriya 400 sakamakon zama a ƙasar ta yankin gabas ta tsakiya ba bisa ka’ida ba, matakin da ke zuwa makwanni bayan dawo da bayar da biza da ƙasar ta yi ga al’ummar Najeriyar.

Rahotanni sun ce manyan hukumomin ƙasar da suka haɗa da na agaji da mai kula da ƴan cirani da masu kula da shige da fice da kuma hukumar yaƙi da safarar mutane baya ga jami’an ofishin babban mai bayar da shawara kan sha’anin tsaro na Najeriyar ne suka tarbi mutanen a filin sauka da tashin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja fadar gwamnatin ƙasar.

Kamar yadda aka ruwaito, mutanen 400 sun ƙunshi mata 90 da kuma maza 310 waɗanda bayanai suka ce wasunsu izinin zamansu a ƙasar ta Haɗaɗɗiyar daular Larabawa ya ƙare amma suka ƙi ficewa yayinda wasunsu suka shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba.

Galibi ƴan Najeriyar kan yi amfani da damar shiga ƙasar da nufin karatu ko kuma cinikayya amma sai su juye zuwa ƙwadago ba tare da takardun izinin yin aiki ba.

Haka zalika akwai bayanan da ke alaƙanta ƴan Najeriyar da aikata ba dai dai ba a ƙasashen musamman na gabas ta tsakiya lamarin da a lokuta da dama kan kaiwa ga korosu gida.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ƙasashe ke tiso ƙeyar ƴan Najeriyar ba, domin kuwa ko a Juma’ar da ta gabata sai da Turkiya ta kwaso ƴan Najeriyar 103 tare da miƙasu ga hukumar NEMA, yayinda ko a karshen shekarar bara, Saudiya ta tiso ƙeyar ƴan Najeriya 264 zuwa gida bayan da ta soke bizar su jim kaɗan bayan saukarsu a filin jirgin saman Sarki Abdul’aziz da ke birnin Jidda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp