Gwamnatin NIjeriya ta bayar da hutun Ranar Haihuwar Annabi S.A.W

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Litinin 16 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar, domin bikin ranar Maulidi.

Cikin wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar cikin gida ta ƙasar, Dr. Magdalene Ajani ya fitar, ya ce ministan ma’aikatar, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.

Al’ummar musulmai a faɗin duniya na gudanar da bukukuwan Maulidi domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

”Gwamnati na taya al’ummar musulman ciki da waɗanda ke zaune a ƙetare murnar zagayowar ranar Maulidin”, in ji sanarwar.

Haka kuma ministan ya yi kira ga musulman ƙasar su yi amfani da lokacin bukukuwan wajen yi wa ƙasar addu’ar zaman lafiya da ci gaban ƙasar.

 

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 29 minutes 58 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 11 minutes 23 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com