Home General An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

An samu raguwar hauhawar farashi a watan Agusta – NBS

Hukumar kididdiga ta Najeriya (NBS) ta ce an samu raguwar hauhawar farashi a ƙasar daga kashi 33.40 a watan Yuni zuwa kashi 32.15 a watan Agusta.

A cewar wani rahoto da NBS ɗin ta fitar ranar Litinin, ta ce an samu raguwar ta kashi 32.15 ne a watan Agustan 2024, yayin da farashin abinci kuma ya kasance a kashi 37.52 a watan na Agusta.

“Alkaluman da muka tattara sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.25 idan aka kwatanta da n watan Yulin 2024,” in ji rahoton.

NBS ta ce farashin kayan abinci a watan Agustan 2024 ya kai kashi 37.52, idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Agustan 2023 na kashi 29.34.

Ta ce an samu hauhawar farashin kayan abincin ne sakamakon tashin farashin kayayyaki kamar burodi da masara da hatsi da dawa da dankalin turawa da rogo da dabino da sauransu.

Hukumar ta ce farashin abinci a watan Agustan 2024 ya kasance a kashi 2.37 wanda ya nuna raguwa da kashi 0.10 idan aka kwatanta da adadin da aka samu a watan Yulin 2024 na kashi 2.47.

Ta ce za a iya danganta raguwar da faɗuwar farashin kayayyaki kamar sikari da ganyen shayi da man gyaɗa da madara da dawa ganyayyaki da sauransu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp