Tinubu ya kai ziyara Maiduguri don jajantawa al’umma iftila’in ambaliya

Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara birnin Maiduguri domin jajantawa al’ummar jihar Borno iftila’in ambaliyar da ya afka musu.

Ziyarar tasa na zuwa ne kwanaki shida bayan mummunar ambaliyar da birnin ya fuskanta wanda rabon a ga haka tun bayan shekara 30 da suka wuce.

Bayan isarsa birnin, kai-tsaye ya garzaya ɗaya daga cikin sansanonin da aka tsugunar da waɗanda lamarin ya ɗaiɗaita domin jajanta musu.

Tinubu ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tallafawa mutanen.

“Ina son tabbatar muku da cewa za mu tallafa muku domin rage raɗadin da kuka shiga sakamakon wannan iftila’i,” in ji Tinubu.

Daga bisani, Tinubu ya ziyarci fadar Mai Martaba Shehun Borno, Alh Umar Garbai Ibn El-Kanemi tare da rakiyar gwamna Babagana Zulum domin jajantawa Basaraken kan al’amarin da ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com