Home General Mutum sama da miliyan biyu ne suka karɓi katin zaɓe a Edo...

Mutum sama da miliyan biyu ne suka karɓi katin zaɓe a Edo – INEC

Hukumar zabe a Najeriya INEC ta sanar da cewa sama da mutum miliyan biyu ne suka karbi katin zaɓensu na dindindin gabanin zaɓen gwamnan jihar Edo da ke tafe ranar Asabar.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta ce mutum 2,629,025 suka yanki katin zaɓe a faɗin jihar.

“An karɓi katuna 2,249,780 yayin da 379,245 sune suka rage ba a karɓa ba zuwa ranar Litinin 16 ga watan Satumban 2024 bayan ƙara wa’adi da muka yi,” in ji INEC.

Hakan ya nuna cewa an karɓi kashi 85.57 na katunan zaɓe a jihar, a cewar hukumar.

Za a gudanar da zaɓen a ɗaukacin rumfunan zaɓe 4,519 da ke faɗin jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp