Home General Tsohon mataimakain shugaban Nijeriya Atiku ya caccaki APC

Tsohon mataimakain shugaban Nijeriya Atiku ya caccaki APC

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya gargaɗi al’ummar jihar Edo da su guji zaɓar ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe ranar Asabar 21 ga watan Satumban, 2024.

Atiku ya bayyana haka ne a shafinsa na X ranar Laraba, inda ya shawarci mazauna jihar da su zaɓi ɗan takara da ya cancanta wanda zai kai jihar gaba.

Ya ce APC ta jefa al’umma cikin mawuyacin hali kuma ba ta jin koke-kokensu.

“A matsayinku na ƴan jihar Edo, ku yi amfani da ƴancinku na yin zaɓe don watsi da rashin shugabanci mai kyau da kuma kawo sauyi. Ku tabbata kun zaɓi cancanta.

“APC ta saba yi wa mutane daɗin baki lokacin yaƙin neman zaɓe, amma da zarar sun yi nasara sai su sauya manufa – jam’iyyar cike take da masu son mulki kawai ba tare da sanya buƙatun al’umma a gaba ba,” in ji Atiku.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriyar ya ce jam’iyyar ta sauka daga tsarin shugabanci nagari tare da yin watsi da buƙatun talakawa.

Ya ce sun jefa ƴan Najeriya cikin wahala da kunshi karkashin jagorancinsu.

Don haka ya buƙaci ƴan jihar ta Edo da su fito su zaɓi ɗan takarar jam’iyyar PDP Dr. Asue Ighodalo wanda a cewarsa shi zai kai jihar gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp