Home General Tsohon mataimakain shugaban Nijeriya Atiku ya caccaki APC

Tsohon mataimakain shugaban Nijeriya Atiku ya caccaki APC

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya gargaɗi al’ummar jihar Edo da su guji zaɓar ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe ranar Asabar 21 ga watan Satumban, 2024.

Atiku ya bayyana haka ne a shafinsa na X ranar Laraba, inda ya shawarci mazauna jihar da su zaɓi ɗan takara da ya cancanta wanda zai kai jihar gaba.

Ya ce APC ta jefa al’umma cikin mawuyacin hali kuma ba ta jin koke-kokensu.

“A matsayinku na ƴan jihar Edo, ku yi amfani da ƴancinku na yin zaɓe don watsi da rashin shugabanci mai kyau da kuma kawo sauyi. Ku tabbata kun zaɓi cancanta.

“APC ta saba yi wa mutane daɗin baki lokacin yaƙin neman zaɓe, amma da zarar sun yi nasara sai su sauya manufa – jam’iyyar cike take da masu son mulki kawai ba tare da sanya buƙatun al’umma a gaba ba,” in ji Atiku.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriyar ya ce jam’iyyar ta sauka daga tsarin shugabanci nagari tare da yin watsi da buƙatun talakawa.

Ya ce sun jefa ƴan Najeriya cikin wahala da kunshi karkashin jagorancinsu.

Don haka ya buƙaci ƴan jihar ta Edo da su fito su zaɓi ɗan takarar jam’iyyar PDP Dr. Asue Ighodalo wanda a cewarsa shi zai kai jihar gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp