Home General Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Old Naira

Gwamnatin Najeriya ta ce ƙasar ta fara sayar da ɗanyen mai da tataccen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Ministan kuɗi da tattalin arzikin na ƙasar, Wale Edun ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ma’aikatar kuɗin ƙasar, ta wallafa a shafinta na X ranar Asabar.

Sanarwar ta ce an fara sayar da ɗanyen man da kuɗin naira ne tun daga ranar ɗaya ga watan Okotoban da muke ciki.

Ministan ya ce hakan na daga cikin matakin da gwamnatin Bola Tinubu ta ɗauka da ake sa ran zai haɓa tattalin arzikin ƙasar da ci gaba da zaman lafiya da dogaro da kai.

Mista Edun ya ce Najeriya za ta ci gaba da bin matakan da suka dace, lura da halin da kasuwannin ɗanyen a duniya ke ciki wajen ciyar da ƙasar gaba.

Matakin na zuwa ne mako tara bayan majalisar zartarwar ƙasar ta amince da ƙudurin Shugaba Tinubu na umartar kamfanin NNPCL ta sayar wa matatar mai ta Dangote da sauran matatun cikin gida ɗanyen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Masu sharhi dai naganin matakin sayar da man da naira maimakon dala zai age farashin kuɗin ƙasar waje a ƙasa, lamarin da suke ganin zai karya farashin dala tare da rage hauhawar farashi a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp