Home AFIRKA Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Shugaban sojin Burkina Faso ya ce yana shirin ƙwace lasisin haƙar ma’adinai da aka bai wa kamfanonin ƙasashen waje domin bayar da su ga ƙungiyoyin haƙar ma’adinai na cikin ƙasar.

Captain Ibrahim Traore ya bayyana haka ne cikin wata hira da wani gidan radiyon ƙasar kan cikar juyin mulkin – da ya kai shi kan karagar mulkin ƙasar – shekara biyu.

Shugaban dai bai bayyana sunayen kamfanonin da zai ƙwace wa lasisin ba.

Kamfanonin haƙar ma’adinai na ƙasashen Australian da Birtaniya da Canada da kuma Rasha na daga cikin kamfanonin da yanzu haka ke aikin haƙar ma’adinin zinare a Burkina Faso.

Matakin na zuwa ne bayan makamancinsa a ƙasashen Mali na Jamhuriyar Nijar, waɗanda dukansu yanzu ke ƙarƙashin mulkin sojoji.

A duka ƙasashen uku an samun ƙaruwar ayyukan masu iƙirarin jihadi, lamarin da ya raba miliyoyin mutane da muhallansu, yake kuma barazana ga ayyukan haƙar ma’adinai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp