Home AFIRKA Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Shugaban sojin Burkina Faso ya ce yana shirin ƙwace lasisin haƙar ma’adinai da aka bai wa kamfanonin ƙasashen waje domin bayar da su ga ƙungiyoyin haƙar ma’adinai na cikin ƙasar.

Captain Ibrahim Traore ya bayyana haka ne cikin wata hira da wani gidan radiyon ƙasar kan cikar juyin mulkin – da ya kai shi kan karagar mulkin ƙasar – shekara biyu.

Shugaban dai bai bayyana sunayen kamfanonin da zai ƙwace wa lasisin ba.

Kamfanonin haƙar ma’adinai na ƙasashen Australian da Birtaniya da Canada da kuma Rasha na daga cikin kamfanonin da yanzu haka ke aikin haƙar ma’adinin zinare a Burkina Faso.

Matakin na zuwa ne bayan makamancinsa a ƙasashen Mali na Jamhuriyar Nijar, waɗanda dukansu yanzu ke ƙarƙashin mulkin sojoji.

A duka ƙasashen uku an samun ƙaruwar ayyukan masu iƙirarin jihadi, lamarin da ya raba miliyoyin mutane da muhallansu, yake kuma barazana ga ayyukan haƙar ma’adinai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp