Home AFIRKA Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Burkina Faso za ta ƙwace lasisin kamfanonin ƙasashen waje masu haƙar ma’adinai

Shugaban sojin Burkina Faso ya ce yana shirin ƙwace lasisin haƙar ma’adinai da aka bai wa kamfanonin ƙasashen waje domin bayar da su ga ƙungiyoyin haƙar ma’adinai na cikin ƙasar.

Captain Ibrahim Traore ya bayyana haka ne cikin wata hira da wani gidan radiyon ƙasar kan cikar juyin mulkin – da ya kai shi kan karagar mulkin ƙasar – shekara biyu.

Shugaban dai bai bayyana sunayen kamfanonin da zai ƙwace wa lasisin ba.

Kamfanonin haƙar ma’adinai na ƙasashen Australian da Birtaniya da Canada da kuma Rasha na daga cikin kamfanonin da yanzu haka ke aikin haƙar ma’adinin zinare a Burkina Faso.

Matakin na zuwa ne bayan makamancinsa a ƙasashen Mali na Jamhuriyar Nijar, waɗanda dukansu yanzu ke ƙarƙashin mulkin sojoji.

A duka ƙasashen uku an samun ƙaruwar ayyukan masu iƙirarin jihadi, lamarin da ya raba miliyoyin mutane da muhallansu, yake kuma barazana ga ayyukan haƙar ma’adinai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp