Home General Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Old Naira

Gwamnatin Najeriya ta ce ƙasar ta fara sayar da ɗanyen mai da tataccen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Ministan kuɗi da tattalin arzikin na ƙasar, Wale Edun ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ma’aikatar kuɗin ƙasar, ta wallafa a shafinta na X ranar Asabar.

Sanarwar ta ce an fara sayar da ɗanyen man da kuɗin naira ne tun daga ranar ɗaya ga watan Okotoban da muke ciki.

Ministan ya ce hakan na daga cikin matakin da gwamnatin Bola Tinubu ta ɗauka da ake sa ran zai haɓa tattalin arzikin ƙasar da ci gaba da zaman lafiya da dogaro da kai.

Mista Edun ya ce Najeriya za ta ci gaba da bin matakan da suka dace, lura da halin da kasuwannin ɗanyen a duniya ke ciki wajen ciyar da ƙasar gaba.

Matakin na zuwa ne mako tara bayan majalisar zartarwar ƙasar ta amince da ƙudurin Shugaba Tinubu na umartar kamfanin NNPCL ta sayar wa matatar mai ta Dangote da sauran matatun cikin gida ɗanyen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Masu sharhi dai naganin matakin sayar da man da naira maimakon dala zai age farashin kuɗin ƙasar waje a ƙasa, lamarin da suke ganin zai karya farashin dala tare da rage hauhawar farashi a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp