Home General Hatsarin kwale-kwalen Neja: An gano gawarwaki aƙalla 141

Hatsarin kwale-kwalen Neja: An gano gawarwaki aƙalla 141

Hukumomi a Najeriya sun ce sun tsamo aƙalla gawarwaki 141 daga cikin mutanen da kwale-kwale ya kife da su ranar Talata a kogin Niger.

Kawo yanzu akwai ragowar mutum 52 da ba a gani ba, waɗanda ake fargabar cewa sun mutu.

Kwale-kwale ta tashi ne daga ƙauyen Gwajibo Mudi, na ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar Kwara ɗauke da fasinjoji aƙalla 300 da ke kan hanyarsu ta zuwa maulidi a garin Gwajibo na jihar Niger mai maƙwabtaka.

Jirgin ya kife ne da fasinjoji fiye da 150 galibinsu mata da ƙananan yara, lamarin da ya jefa al’ummar yankin da dama cikin mawuyacin hali da fargaba.

Tuni dai shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su, tare da bayar da umarnin gudanar da bincike domin gano musabbain hatsarin.

Shugaba Tinubu ya kuma bayar da umarni ga jami’ai su tabbatar masu tuƙa kwale-kwalen ba su saɓa dokar haramcin tafiye-tafiye cikin dare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp