Home General Hatsarin kwale-kwalen Neja: An gano gawarwaki aƙalla 141

Hatsarin kwale-kwalen Neja: An gano gawarwaki aƙalla 141

Hukumomi a Najeriya sun ce sun tsamo aƙalla gawarwaki 141 daga cikin mutanen da kwale-kwale ya kife da su ranar Talata a kogin Niger.

Kawo yanzu akwai ragowar mutum 52 da ba a gani ba, waɗanda ake fargabar cewa sun mutu.

Kwale-kwale ta tashi ne daga ƙauyen Gwajibo Mudi, na ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar Kwara ɗauke da fasinjoji aƙalla 300 da ke kan hanyarsu ta zuwa maulidi a garin Gwajibo na jihar Niger mai maƙwabtaka.

Jirgin ya kife ne da fasinjoji fiye da 150 galibinsu mata da ƙananan yara, lamarin da ya jefa al’ummar yankin da dama cikin mawuyacin hali da fargaba.

Tuni dai shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su, tare da bayar da umarnin gudanar da bincike domin gano musabbain hatsarin.

Shugaba Tinubu ya kuma bayar da umarni ga jami’ai su tabbatar masu tuƙa kwale-kwalen ba su saɓa dokar haramcin tafiye-tafiye cikin dare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp