Home AFIRKA Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a...

Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a Congo

Aƙalla mutane 78 ake fargabar sun rasa rayukansu a Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo bayan nutsewar wani jirgin ruwa yayin da yake ƙoƙarin ketara tabkin Kivu ɗauke da fasinjoji 278.

Gwamnan Lardin Kudancin Kivu da ke gabashin Jamhuriyar Congon Jean Jacques ne ya tabbatar da adadin mamatan na mutane 78, da kuma yawan fasinjojin kusan 300 da ke cikin jirgin da ya nutse.

Sai dai ya ce basu kammala tantance adadin rayukan da suka salwanta a haɗarin ba, aikin da ya ce zai ɗauki jami’an ceto aƙalla kwanaki uku suna yi.

Har zuwa daren jiya dai an riƙa samun bayanai masu cin karo da juna akan yawan waɗanda haɗarin jirgin ruwan ya rutsa da su, domin a yayin da mahukuntan lardin Kivu suka bayar da nasu alƙaluman, takwarorinsu na arewacin Lardin Kivun cewa suka yi mutane 28 suka rasa rayukansu, yayin da wasu 58 suka tsira.

Ɗaukar fasinjoji fiye da kima ke kan gaba a cikin dalilan dake haddasa yawaitar nutsewar jiragen ruwa a Jamhuriyar Congo, lamarin da ake kyautata zaton ko a wannan karon shi ne musababbin haɗarin da ya auku.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp