Home AFIRKA Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a...

Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a Congo

Aƙalla mutane 78 ake fargabar sun rasa rayukansu a Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo bayan nutsewar wani jirgin ruwa yayin da yake ƙoƙarin ketara tabkin Kivu ɗauke da fasinjoji 278.

Gwamnan Lardin Kudancin Kivu da ke gabashin Jamhuriyar Congon Jean Jacques ne ya tabbatar da adadin mamatan na mutane 78, da kuma yawan fasinjojin kusan 300 da ke cikin jirgin da ya nutse.

Sai dai ya ce basu kammala tantance adadin rayukan da suka salwanta a haɗarin ba, aikin da ya ce zai ɗauki jami’an ceto aƙalla kwanaki uku suna yi.

Har zuwa daren jiya dai an riƙa samun bayanai masu cin karo da juna akan yawan waɗanda haɗarin jirgin ruwan ya rutsa da su, domin a yayin da mahukuntan lardin Kivu suka bayar da nasu alƙaluman, takwarorinsu na arewacin Lardin Kivun cewa suka yi mutane 28 suka rasa rayukansu, yayin da wasu 58 suka tsira.

Ɗaukar fasinjoji fiye da kima ke kan gaba a cikin dalilan dake haddasa yawaitar nutsewar jiragen ruwa a Jamhuriyar Congo, lamarin da ake kyautata zaton ko a wannan karon shi ne musababbin haɗarin da ya auku.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp