Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun yi kira ga al’ummar ƙasar su kasance a faɗake bayan da wasu koguna suka cika maƙil har su ke barazanar tumbatsa, a yayin da kasar ke ƙoƙarin murmurewa daga ambaliyar da ta kashe mutane sama da ɗari 5 kwanakin baya.

Fira minista, Allamaye Alina ya ce ruwan kogin Chari ya ƙaru da sama da mita 8, kwatankwacin ƙafa 26 a cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Babban birnin Chadi, N’Djamena,  yana kusa ne da inda kogunan Logon da Chari suka yi magama, kuma dukannin kogunan sun cika sakamakoln mamakon ruwan sama da ake ta yi.

Tun a watan Yuli ƙasar ta fuskanci mummunar ambaliya, wadda ta lalata gidaje dubu dari da 64 da kadada dubu ɗari 2 da 50 na filayen noma.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp