Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun yi kira ga al’ummar ƙasar su kasance a faɗake bayan da wasu koguna suka cika maƙil har su ke barazanar tumbatsa, a yayin da kasar ke ƙoƙarin murmurewa daga ambaliyar da ta kashe mutane sama da ɗari 5 kwanakin baya.

Fira minista, Allamaye Alina ya ce ruwan kogin Chari ya ƙaru da sama da mita 8, kwatankwacin ƙafa 26 a cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Babban birnin Chadi, N’Djamena,  yana kusa ne da inda kogunan Logon da Chari suka yi magama, kuma dukannin kogunan sun cika sakamakoln mamakon ruwan sama da ake ta yi.

Tun a watan Yuli ƙasar ta fuskanci mummunar ambaliya, wadda ta lalata gidaje dubu dari da 64 da kadada dubu ɗari 2 da 50 na filayen noma.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp