Home General Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Gwamnan Jihar Ribas Similary Fubara Ya Bukaci Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar da su kasance Masu Sanya kishin Al’umma a gabansu

A Wani kwarya kawaryar Bikin da ya gudana a Dakin taro na gidan Gwamnatin Jihar Ribas, Gwamnan yace Zaben da akayi na Kananan Hukumomi a Jihar ya Bude wata Sabuwar Sabon Shafi na Sabuwar Jihar Ribas

Ya Kara Da Cewa Yanzu Jihar Ribas ta kasance Jiha Mai Yanci da Kuma Cin gashin kanta Wadda Kuma Zata Cigaba da zama da kafafuwanta.

Bayanin Gwamnan Jihar ta Ribas dai na zama Wani sako ga Tsohon Gwamnan Jihar ta Ribas Nyesom wike Dake zama Tsohon Mai Gidan Gwamnan na Yanzu Wanda Kuma Suka raba gari tin Kafin tafiya Tayi nisa.

Gwamnan yana Cewa Mulkin mallaka da Kuma San zuciya ya zama tarihi a Jihar Ribas Kuma zamu Cigaba da Samar da ayyukan raya Kasa tare da Hadin guiwar Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar ta Ribas

Zaben Wanda ya kasance Mai cike da Kalubale musamman ta Fuskar Tsaro Kasancewar jami’an Tsaro na Yan Sanda sun janye jiki daga bayar da Tsaro a Zaben da ya Gabata.

Sai dai duk da haka Gwamnan ya Tabbatar da karfin ikonsa na Tabbatar da Gudanar da Zaben da Hukumar Zaben Jihar ta shirya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp