Home General Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Gwamnan Jihar Ribas Similary Fubara Ya Bukaci Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar da su kasance Masu Sanya kishin Al’umma a gabansu

A Wani kwarya kawaryar Bikin da ya gudana a Dakin taro na gidan Gwamnatin Jihar Ribas, Gwamnan yace Zaben da akayi na Kananan Hukumomi a Jihar ya Bude wata Sabuwar Sabon Shafi na Sabuwar Jihar Ribas

Ya Kara Da Cewa Yanzu Jihar Ribas ta kasance Jiha Mai Yanci da Kuma Cin gashin kanta Wadda Kuma Zata Cigaba da zama da kafafuwanta.

Bayanin Gwamnan Jihar ta Ribas dai na zama Wani sako ga Tsohon Gwamnan Jihar ta Ribas Nyesom wike Dake zama Tsohon Mai Gidan Gwamnan na Yanzu Wanda Kuma Suka raba gari tin Kafin tafiya Tayi nisa.

Gwamnan yana Cewa Mulkin mallaka da Kuma San zuciya ya zama tarihi a Jihar Ribas Kuma zamu Cigaba da Samar da ayyukan raya Kasa tare da Hadin guiwar Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar ta Ribas

Zaben Wanda ya kasance Mai cike da Kalubale musamman ta Fuskar Tsaro Kasancewar jami’an Tsaro na Yan Sanda sun janye jiki daga bayar da Tsaro a Zaben da ya Gabata.

Sai dai duk da haka Gwamnan ya Tabbatar da karfin ikonsa na Tabbatar da Gudanar da Zaben da Hukumar Zaben Jihar ta shirya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp