Home General Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Fubara ya gana da sabbin zababbun shuwagabannin kananan hukumomin Ribas

Gwamnan Jihar Ribas Similary Fubara Ya Bukaci Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar da su kasance Masu Sanya kishin Al’umma a gabansu

A Wani kwarya kawaryar Bikin da ya gudana a Dakin taro na gidan Gwamnatin Jihar Ribas, Gwamnan yace Zaben da akayi na Kananan Hukumomi a Jihar ya Bude wata Sabuwar Sabon Shafi na Sabuwar Jihar Ribas

Ya Kara Da Cewa Yanzu Jihar Ribas ta kasance Jiha Mai Yanci da Kuma Cin gashin kanta Wadda Kuma Zata Cigaba da zama da kafafuwanta.

Bayanin Gwamnan Jihar ta Ribas dai na zama Wani sako ga Tsohon Gwamnan Jihar ta Ribas Nyesom wike Dake zama Tsohon Mai Gidan Gwamnan na Yanzu Wanda Kuma Suka raba gari tin Kafin tafiya Tayi nisa.

Gwamnan yana Cewa Mulkin mallaka da Kuma San zuciya ya zama tarihi a Jihar Ribas Kuma zamu Cigaba da Samar da ayyukan raya Kasa tare da Hadin guiwar Sabbin Zababbun Shugabannin Kananan Hukumomi 23 da aka zaba a Jihar ta Ribas

Zaben Wanda ya kasance Mai cike da Kalubale musamman ta Fuskar Tsaro Kasancewar jami’an Tsaro na Yan Sanda sun janye jiki daga bayar da Tsaro a Zaben da ya Gabata.

Sai dai duk da haka Gwamnan ya Tabbatar da karfin ikonsa na Tabbatar da Gudanar da Zaben da Hukumar Zaben Jihar ta shirya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp