Home Labarai Shugabanni ba su da rigar kariya a Musulunci – Pantami

Shugabanni ba su da rigar kariya a Musulunci – Pantami

Kashifu pantami

Tsohon ministan sadarwa a Najeriya, farfesa Isa Ali Pantami ya yi kira da a yi watsi da tsarin ba shugabanni rigar kariya.

Pantami ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Abuja a wajen taron shekara-shekara na cibiyar Musulmi wato the Muslim Congress (TMC) mai taken; ‘Gina ingantacciyar ƙasa: Nauyi ne kan shugabanni da mabiya domin tuna ranar ƴancin Najeriya na 64.

“A Musulunci, babu wata rigar kariya domin kariyar za ta ba mutum wata dama ce kawai a lokacin da yake shugabanci, wanda ba za ka samu ba, bayan ka bar ofis. Wasu lokutan kariyar na da kyau, amma a wasu lokutan hakan na jawo maka matsaloli da yawa ne,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa, “da zarar ka bar ofis bayan shekara huɗu ko takwas sai ka ga ana ƙalubalantakarka da tuhume-tuhume da dama, wasu har guda 120 ma. Don haka kariyar ba ta hana mutum fuskantar shari’a, kawai tana jawo kawo jinkiri ne da kuma ba mutum damar ƙara aikata wasu laifukan.

“A shari’ar Musulunci babu wata rigar kariya. Da shugaba da mabiya kowa zai iya fuskantar shari’a, kuma dole ya je ya kare kansa. An yi wa Ali ibn Abi Talib da Umar ibn Khatab suna Khalifanci. Don haka yana da kyau a samar da daidaito a wajen shari’a,” in ji Pantami.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp