Home Labarai Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya NIS ta bukaci jami’anta da su sake zage dantse gami da inganta ayyukan su.

Shugabar hukumar CSI Kemi Nanna Nandap ce ta bayyana hakan yayin taron bikin daga likkafar jami’an hukumar 450 a shalkwatar hukumar dake jihar Kano.

CSI Nandap wadda ta sami wakilcin shugaban hukumar reshen jihar Kano Ibrahim Muhammad Abubakar lafiya ta bayyana muhimmanci Karin girman gami da sake inganta ayyukan hukumar ga jami’an

Abubakar lafiya ya kara da cewa hukumar ta yi wannan Karin girma ne ga Jami’an saboda hazaka da mayar da hankulansu akan aiki, ba wai dan sun fi kowa bane.

“Wannan Karin girma muka fada musu akan cewa, bawai ko sun fi wasu bane saboda hazakar su ne da kuma kwarewar su a wurin aiki, da kuma suka ci jarrabawa shine Allah ya basu wannan matsayin da yanzu suke kai”

“Muna yi musu murna, muna kuma jan hankalin su da su sake daure damararsu, kasancewar akwai Jan aiki a gabansu a wannan ma’aikata ta shige da fice.

Haka kuma shugaban hukumar ya sake zaburar da jami’an hukumar wajen sanya idanu, don magance harkokin safarar mutane dake addabar nahiyar Afirka da ma kasa baki daya.

Inda ya ce hukumar ta shirya tsaf domin sake fadada ayyukanta a kananan hukumomin jihar Kano 44 don kawo karshen wannan matsala.

“Yanzu haka muna da wani shiri da muke jiran umarni daga sama, domin fara wani aiki kafa shingen bincike a dukkanin mashigar jihar kano da ko wacce kusurwa”

Yace sun dauki wannan mataki domin kada ma wadanda ake safarar a sami damar fita ko shigo da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp