Home General Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Hukumar Kula da Albarkatun Ruwa ta Najeriya (NIHSA), ta ta shawarci ƴan Najeriya da ke zaune a gaɓar tekuna da su bar yankunan cikin gaggawa.

Darakta-janar na hukumar, Umar Mohammed ne ya yi wannan gargaɗi a wata sanarwa, inda ya ce ruwan da ke tekun Benue ya kai matakin ambaliya saboda ƙaruwar mamakon ruwan sama.

Ya kuma buƙaci mutanen da ke zaune a gaɓar tekun Neja da su ma su bar yankin, inda ya ce hukumomin madatsun ruwa na Kainji da Jebba na aikin kare afkuwar ambaliya.

Mohammed ya yi kira ga ƴan Najeriya da su bayar da haɗin-kai ga hukumomin agaji domin ganin an rage barazanar ambaliya.

A baya-bayan nan, gwamnati ta gargaɗi ƴan Najeriya da su tashi daga wuraren da ke da haɗarin afkawa cikin ambaliya sakamakon sake ruwan madatsar Lagdo daga Kamaru.

Wannan ya zo ne bayan mummunar ambaliya da aka fuskanta a Maiduguri sakamakon ɓallewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya kashe mutane 37 tare da ɗaiɗaita miliyoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp