Home General Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Hukumar Kula da Albarkatun Ruwa ta Najeriya (NIHSA), ta ta shawarci ƴan Najeriya da ke zaune a gaɓar tekuna da su bar yankunan cikin gaggawa.

Darakta-janar na hukumar, Umar Mohammed ne ya yi wannan gargaɗi a wata sanarwa, inda ya ce ruwan da ke tekun Benue ya kai matakin ambaliya saboda ƙaruwar mamakon ruwan sama.

Ya kuma buƙaci mutanen da ke zaune a gaɓar tekun Neja da su ma su bar yankin, inda ya ce hukumomin madatsun ruwa na Kainji da Jebba na aikin kare afkuwar ambaliya.

Mohammed ya yi kira ga ƴan Najeriya da su bayar da haɗin-kai ga hukumomin agaji domin ganin an rage barazanar ambaliya.

A baya-bayan nan, gwamnati ta gargaɗi ƴan Najeriya da su tashi daga wuraren da ke da haɗarin afkawa cikin ambaliya sakamakon sake ruwan madatsar Lagdo daga Kamaru.

Wannan ya zo ne bayan mummunar ambaliya da aka fuskanta a Maiduguri sakamakon ɓallewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya kashe mutane 37 tare da ɗaiɗaita miliyoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp