Home Labarai Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da cewa za a gudanar da zaben kananan hukumomi kamar yadda aka tsara a ranar Asabar 26 ga watan Oktoba, 2024, duk da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na hana hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC gudanar da zaben.

Wannan matsaya ta biyo bayan hukuncin da mai shari’a Simon Amobeda na babbar kotun tarayya da ke Kano ya yanke a ranar Talata,

Kotu tace wadanda aka bawa mukamin shugabannin hukumar basu cancanta saboda sun kasance magoya bayan jamiyyar NNPP mai mulkin Kano, dan haka kotun tace wadannan mutane basu da damar gudanar da zaben Ƙananan.
Sai dai gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na ci gaba da gudanar da zaben, ko da kuwa hukumomin tsaro irin na ‘yan sanda ba sa iya ba da kariya.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Dala, ya soki hukuncin kotun, yana mai cewa ya sabawa umarnin da mai shari’a Nura Ma’aji ya bayar a baya, wanda ya haramtawa jam’iyyun siyasa 19 ciki har da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kalubalantar zabe.

“Hukuncin da kotun tarayya ta yanke na tsige shugaban KANSIEC ya ci karo da hukuncin da Mai shari’a Ma’aji ya yanke na hana jam’iyyun siyasa kutsawa cikin harkokin zabe,” in ji Dala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp