Home General Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a...

Peter Obi ya bukaci yin bincike kan tauye hakkin kananan yara a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar adawa ta LP a Najeriya, Peter Obi ya yi kira ga mahukuntar ƙasar, musamman ministan shari’a da rundunar ‘yansanda da DSS da kuma hukumar kare haƙƙin bil-adama su gudanar da cikakken bincike kan ”azabtarwar da aka yi wa ƙananan yaran da aka gurfanar a gaban kotu bisa zargin cin amanar ƙasa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Obi ya ce bidiyon yaran da aka yaɗa a gaban kotu abin tayar da hankali ne.

”Halin da yaran ke ciki na yunwa da galabaita abin tayar da hankali ne ga duk wani mai hankali a ƙasar nan”, in ji shi.

A yau ne dai ‘yansandan Najeriya suka gabatar da wasu mutane ciki har da ƙananan yara a gaban kotu bisa zargin laifuka masu yawa ciki har da cin amanar ƙasa, kimanin wata uku bayan kamasu.

Yadda aka gabatar da yaran ya janyo ka-ce-na-ce a faɗin ƙasar, musamman yadda aka ga wasu daga cikin ƙananna yaran cikin mawuyacin hali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp