Home General COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana mutuwar shugaban rundunar sojin Nijeriya Laftanar Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, wanda ya mutu yana da shekaru 56 a duniya.

Wannan na cikin wata sanarwa da masawarci na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fita, aka raba manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Taoreed Abiodun Lagbaja ya mutu a daren talata bayan fama da rashin lafiya.

An haifi Taoreed Lagbaja a 28 ga watan Fabrerun 1968, sannan shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad ya nadashi matsayin Hafsan sojojin Najeriya a ranar 19 ga watan Yunin 2023.

ya fara aiki da rundunar sojin kasar ne bayan daukar horo a kwalejin sojojin kasar ta Nigerian Defence Academy a 1987, in da a ranar 19 ga watan satumba 1992, ya fito a matsayin Second Lieutenant rukuni na 39 (39th Regular Course).

a yayin aikinsa Lt. General Lagbaja ya nuna gogewa da shugabanci na gari gami da sadaukar a matsayin kwamandan bataliya ta 72 rukunin sojoji na musamman.

ya kuma taimaka matuka wajen gudanar da ayyukan tsaron cikin gida, wanda ya hadar da jagarantar dakarun OPERATION ZAKI a jihar Benue, Lafiya Dole a jihar Borno, Udoka a kudancin Nijeriya, da Operation Forest Sanity a yankin Jihohin Kaduna da Niger.

haka kuma ya halarci kwalejin sojoji ta Amurka in da ya yi sami digiri na II a dabaru wato “Strategic Studies” wanda hakan ya bashi damar nuna sadaukarwa da kwarewa gami na son cigaban harkokin shugabancia a ayyukan soji.

Lt. General Lagbaja yana da Mata daya Mai suna Mariya da ‘ya’ya guda biyu.

daga bisani shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da rundunar sojin Nijeriya bisa wannan rashi ya kuma yi masa addu’a da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp