Home General Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ce ba ya yi wa Tinubu hassada, inda ya ce ya jefa ƴan Najeriya cikin kunci.

Ɗan takarar shugaban ƙasar karkashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, na mayar da martani kan kalamai da fadar shugaban Najeriyar ta yi cewa yana ƙyashi tare da baƙin ciki da matsayin Shugaba Bola Tinubu na shugaban ƙasa.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, ya soki Atiku kan ci gaba da sukar tsare-tsaren tattalin arzikin da shugaban, maimakon mayar da hankali kan matsalolin jam’iyyarsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar dai ya sha sukar tsare-tsare da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, musamman na tattalin arziki, inda ya ce babu abin da za su haifar illa jefa ƴan Najeriya cikin kunci da wahala.

Wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan yaɗa labarai Phrank Shaibu ya fitar ranar Litinin, Atiku ya ce sai Tinubu ya aiwatar da tsare-tsare kafin yake duba illolin da za su haifar.

“Tinubu bai shiryawa mulki ba. Sai ya aiwatar da abu kafin yake duba illarsa daga baya. Wannan shi ya sa ya sanar da janye tallafin man fetur ba tare da kawo abin da zai rage wa ƴan ƙasar raɗaɗi ba.

“Abin mamaki ne a yi iƙirarin cewa Atiku na kyashin Tinubu. Ba zai yi hassada da Tinubu ba saboda irin kunci da ya jefa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Atiku ya ce babu wani adalin shugaba wanda yake da zimmar ganin ƴan Najeriya cikin walwala da zai yi hassada da irin gallazawa da ake yi musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp