Hukumar zaɓen Najeriya ta ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammcin Najeriya.

Sakamakon zaɓen ya nuna cewa mista Aiyedatiwa – wanda shi ne gwamnan jihar mai ci – ya cinye duka ƙananan hukumomin jihar 18.

Babban jami’in tattara sakamakon, Farfesa Olayemi Akinwunmi, shugaban jami’an gwamnatin tarayya da ke Lokoja, ya ce Aiyedatiwa ya smu ƙuri’a 366,781, yayin da Agboola Ajayi na PDP ya samu ƙuri’a 117, 845, sai jam’iyyar LP da ta samu ƙuri’a 1,162.

”Bayan samu ƙuri’u mafiya rinjaye a zaɓen tare da cika duka sharuɗan da hukumar zaɓe ta ginda, a nan nake ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe wannan zaɓe”, in ji Farfesa Akinwunmi.

an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, kuma babu labarin wani tashin hankali a sassan jihar a yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaɓen.

A ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba ne hukumar zaɓen Najeriya ta gudanar da zaɓen gwamnan jihar.

Hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta ce mutum miliyan 2,053,061 ne suka yi rajistar zaɓe a faɗin jihar, yayin da matasa ke da kashi 35.41 cikin 100 na waɗanda suka yi rajistar zaɓen.

Jihar Ondo da ke yankin kudu maso yammacin Najeriya na da ƙananan hukumomi 18.

Jam’iyyu 18 ne suka fafata a zaɓen na yau, sai dai ana ganin fafatawar ta fi zafi tsakanin ‘yan takara biyu, wato gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa na APC da Agboola Ajayi na PDP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp