Hukumar zaɓen Najeriya ta ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammcin Najeriya.

Sakamakon zaɓen ya nuna cewa mista Aiyedatiwa – wanda shi ne gwamnan jihar mai ci – ya cinye duka ƙananan hukumomin jihar 18.

Babban jami’in tattara sakamakon, Farfesa Olayemi Akinwunmi, shugaban jami’an gwamnatin tarayya da ke Lokoja, ya ce Aiyedatiwa ya smu ƙuri’a 366,781, yayin da Agboola Ajayi na PDP ya samu ƙuri’a 117, 845, sai jam’iyyar LP da ta samu ƙuri’a 1,162.

”Bayan samu ƙuri’u mafiya rinjaye a zaɓen tare da cika duka sharuɗan da hukumar zaɓe ta ginda, a nan nake ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe wannan zaɓe”, in ji Farfesa Akinwunmi.

an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, kuma babu labarin wani tashin hankali a sassan jihar a yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaɓen.

A ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba ne hukumar zaɓen Najeriya ta gudanar da zaɓen gwamnan jihar.

Hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta ce mutum miliyan 2,053,061 ne suka yi rajistar zaɓe a faɗin jihar, yayin da matasa ke da kashi 35.41 cikin 100 na waɗanda suka yi rajistar zaɓen.

Jihar Ondo da ke yankin kudu maso yammacin Najeriya na da ƙananan hukumomi 18.

Jam’iyyu 18 ne suka fafata a zaɓen na yau, sai dai ana ganin fafatawar ta fi zafi tsakanin ‘yan takara biyu, wato gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa na APC da Agboola Ajayi na PDP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp