Hukumar zaɓen Najeriya ta ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammcin Najeriya.

Sakamakon zaɓen ya nuna cewa mista Aiyedatiwa – wanda shi ne gwamnan jihar mai ci – ya cinye duka ƙananan hukumomin jihar 18.

Babban jami’in tattara sakamakon, Farfesa Olayemi Akinwunmi, shugaban jami’an gwamnatin tarayya da ke Lokoja, ya ce Aiyedatiwa ya smu ƙuri’a 366,781, yayin da Agboola Ajayi na PDP ya samu ƙuri’a 117, 845, sai jam’iyyar LP da ta samu ƙuri’a 1,162.

”Bayan samu ƙuri’u mafiya rinjaye a zaɓen tare da cika duka sharuɗan da hukumar zaɓe ta ginda, a nan nake ayyana Lucky Aiyedatiwa na APC a matsayin wanda ya lashe wannan zaɓe”, in ji Farfesa Akinwunmi.

an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, kuma babu labarin wani tashin hankali a sassan jihar a yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaɓen.

A ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba ne hukumar zaɓen Najeriya ta gudanar da zaɓen gwamnan jihar.

Hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta ce mutum miliyan 2,053,061 ne suka yi rajistar zaɓe a faɗin jihar, yayin da matasa ke da kashi 35.41 cikin 100 na waɗanda suka yi rajistar zaɓen.

Jihar Ondo da ke yankin kudu maso yammacin Najeriya na da ƙananan hukumomi 18.

Jam’iyyu 18 ne suka fafata a zaɓen na yau, sai dai ana ganin fafatawar ta fi zafi tsakanin ‘yan takara biyu, wato gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa na APC da Agboola Ajayi na PDP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp