Ƙudirin da zai yi wa kundin tsarin mulkin Najeriya kwaskwarima domin bai wa ƴan ƙasar mazauna ƙasashen waje damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓe ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai a ranar Laraba.
Ƙudirin wanda shugaban majalisar, Abbas Tajudeen da Sodeeq Abdullahi suka ɗauki nauyinsa, na neman yin gyara ga dokar zaɓe ta 2022 domin a bayar da dama ga ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje su kaɗa ƙuri’a.
An amince da karanta ƙudurin karo na biyu a watan Yuli, kuma an miƙa shi ga kwamitin da ke kula da harkokin zaɓe don ci gaba da nazarinsa.
Sai dai bayan tsallake karatu na biyu a ranar Talata, an miƙa shi ga kwamitin gyaran kundin tsarin mulki don ci gaba tattaunawa a kansa.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1490 days 14 hours 28 minutes 50 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1472 days 16 hours 10 minutes 15 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com