Home General An sake zaɓar Okonjo-Iweala shugabar WTO a wa’adi na biyu

An sake zaɓar Okonjo-Iweala shugabar WTO a wa’adi na biyu

Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, WTO ta sake zaɓar Dakta Ngozi Okonjo-Iweala a matsayin shugabanta a wa’adin mulki na biyu, inda za ta ci gaba da jagorantar ƙungiyar har zuwa 2029.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da harkokin cinikayyar duniya ke cikin wani mawuyacin yanayi.

A farkon makon nan zaɓaɓɓen shugaban Amurka, Donald Trump ya ce zai ƙaƙaba sabbin haraje-harajen cinikayya da ƙasashen Canada da Mexico da China idan ya kama aiki cikin watan Janairu.

A lokacin wa’adin mulkinsa na farko, Donald Trump ya yi yunƙurin hana Ms Okonjo-Iweala samun matsayin, inda ta samu nasarar ɗarewa muƙamin bayan Joe Biden ya zama shugaban Amurka.

Babban abin tambaya a yanzu shi ne irin tasirin da ƙungiyoyin kasuwanci irin WTO za su yi, a daidai lokacin da manyan ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki ke ƙara samun saɓanin kasuwanci.

Ga kuma batun yaƙin Ukraine da ya haifar da ƙarin takunkuman kasuwancin tsakanin wasu manyan ƙasashe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp