Tinubu ya taya Mahama murnar samun nasarar zaɓen Ghana

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya taya ɗan takarar shugaban ƙasar Ghana na jam’iyyar NDC mai hamayya, John Dramani Mahama, murnar nasarar da ya samu a zaɓen ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da mataimakin shugaban ƙasa Muhammadu Bawumia ya amince da shan kaye.

Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar, ta ce shugaba Tinubu ya yi fatan cewa hulɗa tsakanin ƙasashen biyu za ta ƙaru da kuma ganin kwanciyar hankali a faɗin ƙasashen ƙungiyar Ecowas.

Tinubu ya jinjinawa ƴan Ghana ta yadda suka fito suka yi zaɓe, inda a ɗaya gefen ya kuma yaba wa halin dattako da Bawumia ya nuna na amsa shan kaye tun kafin hukumar zaɓen Ghana ta sanar da sakamakon.

Har yanzu dai hukumar zaɓen ƙasar ba ta fara bayyana sakamakon zaɓen a hukumance ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 14 hours 40 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 21 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com