Home General Tinubu ya taya Mahama murnar samun nasarar zaɓen Ghana

Tinubu ya taya Mahama murnar samun nasarar zaɓen Ghana

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya taya ɗan takarar shugaban ƙasar Ghana na jam’iyyar NDC mai hamayya, John Dramani Mahama, murnar nasarar da ya samu a zaɓen ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da mataimakin shugaban ƙasa Muhammadu Bawumia ya amince da shan kaye.

Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar, ta ce shugaba Tinubu ya yi fatan cewa hulɗa tsakanin ƙasashen biyu za ta ƙaru da kuma ganin kwanciyar hankali a faɗin ƙasashen ƙungiyar Ecowas.

Tinubu ya jinjinawa ƴan Ghana ta yadda suka fito suka yi zaɓe, inda a ɗaya gefen ya kuma yaba wa halin dattako da Bawumia ya nuna na amsa shan kaye tun kafin hukumar zaɓen Ghana ta sanar da sakamakon.

Har yanzu dai hukumar zaɓen ƙasar ba ta fara bayyana sakamakon zaɓen a hukumance ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp