Home General Gwamnati ta ƙara kuɗin tallafin lantarki da take biya — NERC

Gwamnati ta ƙara kuɗin tallafin lantarki da take biya — NERC

Kuɗaɗen da gwamnatin Najeriya ke biya a matsayin tallafin lantarki ya ƙaru zuwa naira biliyan 199.64 a watan Disamban 2024, kamar yadda alƙaluma daga hukumar kula da lantarki NERC suka nuna.

Tashar Channels ta ruwaito daga wani rahoto da hukumar ta fitar cewa kuɗin tallafin ya ƙaru da kashi 2.76 wato naira biliyan 199.64 a wannan watan na Disamban, daga naira biliyan 194.26 a watan Nuwamban bana.

Hukumar NERC ta ce an samu ƙarin ne saboda faɗuwar darajar naira, kasancewar an ƙiyasta darajar dala ne a naira 1,687.45 a kasafin kuɗin kasar, da hauhawar farashin kayayyaki da ya ƙaru zuwa kashi 33.9.

Rahoton ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ba ta canja farashin lantarki ba a ɗan tsakankanin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp