Gwamnatin tarayya ta bayar da hutun aiki a ranar Laraba 25 da Alhamis 26 ga watan Disamban 2024 domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da babban sakatariyar ma’aikatan, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.
Tunji-Ojo ya miƙa gaisuwarsa ga ƴan Najeriya, sannan ya yi kira gare su yi amfani da lokacin bukuwan domin nuna ƙauna da kira ga zaman lafiya.
Ya ce gwamnatin Najeriya a shirye take ta cigaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban ƙasar, sannan ya taya kiristoci murna, tare da musu fatan alheri.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 14 hours 42 minutes 3 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 16 hours 23 minutes 28 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com