Home General Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce daga yanzu ma’aikatan jihar za a fara biyan ma’aikatan jihar da sabon tsarin albashin.

Ya kuma ce gwamna Dauda Lawal ya amince da ƙarin albashi ko kuma alawus na ƙarin wata ɗaya ga ma’aikata a faɗin jihar.

“Wannan shi ne irinsa na farko a tarihin Zamfara, wanda kuma gwamna Dauda Lawal ya biya a cikin watan Disamba,” in ji sanarwar.

Kakakin gwamnan ya ce dukkan ma’aikatan jihar, ciki har da waɗanda suka yi ritaya za su samu kashi 30 na alawus.

Gwamnan Dauda Lawal ya ce ya amince da albashi mafi ƙanƙantan da kuma alawus ne domin taimakawa ma’aikatan jihar a wannan lokaci na bukukuwan karshen shekara da kuma ƙara musu karfin gwiwa wajen aiki tukuru wajen kai jihar gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp