Zamu kwace mulki a hannun APC – Jam’iyyar PDP

Babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya ta PDP ta ce za su samu ƙarin gwamnoni a zaɓen 2027, ƙari a kan guda 12 da take da su a yanzu, sannan ta karɓe mulkin ƙasar.

Jagororin jam’iyyar ne suka bayyaka haka a lokacin da suka kai ziyara ga Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, kamar yadda tashar Channels ta wallafa a shafin ta.

Ma’ajin jam’iyyar, Alhaji Ahmed Yayare ne bayyana hakan a madadin jam’iyyar, inda ya ce yanayin yadda ƙasar ke fama da taɓarɓarewar tattalin arziki ne ya sa PDP za ta samu sauƙin samun nasara a 2027.

Ya ƙara da cewa, “babu abin da zai hana PDP karɓe mulkin ƙasar. Yanzu APC ba ta abin da za ta yi kamfe da shi saboda yunwa da talauci ya yi a ƙasar. Idan suka fita kamfe sai an jefe su.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 14 hours 7 minutes 59 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 15 hours 49 minutes 24 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com