Nahiyar Afirka za ta iya riƙe kanta da kanta — Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce nahiyar Afirka na da duk abin da ake buƙata domin riƙe kanta da kanta.

Tinubu ya bayyana haka ne a birnin Abu Dhabi na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a ranar Litinin lokacin da yake ganawa da Shugaban Ƙasar Rwanda, Paul Kagame.

Tinubu ya wallafa a shafinsa na X cewa, “a yammacin yau a makon taron ci gaba na Abu Dhabi, na samu ganawa da Shugaban Ƙasar Rwanda, Paul Kagame.

“Nahiyar Afirka na da duk abin da ake buƙata domin ciyar da kanta gaba. Muna da ɗimbin arziki da mutane da ƙwarewa. Dole mu yi nazari a tsakaninmu domin inganta hanyoyin kasuwancin ƙasashen Afirka domin amfanin nahiyarmu da mutane. Yanzu ne lokacin da Afrka za ta dara.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 13 hours 11 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 14 hours 52 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com