Home AFIRKA Nahiyar Afirka za ta iya riƙe kanta da kanta — Tinubu

Nahiyar Afirka za ta iya riƙe kanta da kanta — Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce nahiyar Afirka na da duk abin da ake buƙata domin riƙe kanta da kanta.

Tinubu ya bayyana haka ne a birnin Abu Dhabi na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a ranar Litinin lokacin da yake ganawa da Shugaban Ƙasar Rwanda, Paul Kagame.

Tinubu ya wallafa a shafinsa na X cewa, “a yammacin yau a makon taron ci gaba na Abu Dhabi, na samu ganawa da Shugaban Ƙasar Rwanda, Paul Kagame.

“Nahiyar Afirka na da duk abin da ake buƙata domin ciyar da kanta gaba. Muna da ɗimbin arziki da mutane da ƙwarewa. Dole mu yi nazari a tsakaninmu domin inganta hanyoyin kasuwancin ƙasashen Afirka domin amfanin nahiyarmu da mutane. Yanzu ne lokacin da Afrka za ta dara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp