Home General Arewa Na Da Hanyoyin Tara Haraji Daga VAT Da Dama – CNG

Arewa Na Da Hanyoyin Tara Haraji Daga VAT Da Dama – CNG

Gamayyar kungiyoyin arewacin Najeriya CNG, ta ce yankin arewa na da dimbin hanyoyin tara harajin da za su cike gurbin kudurin dokar sabunta haraji da ke gaban majalisar dattawa.

Wannan ya biyo bayan zama da kwararru kan hanyoyin raya tattalin arziki, da kungiyar ta yi a Abuja don neman mafita idan kudurin ya samu nasara.

CNG wacce ta sake nanata bukatar dakatar da kudurin don yi ma sa garambawul da zai dace da muradun kowane yanki, ta ce hakkin ya rataya a kan ‘yan Arewa a majalisa su tabbatar ba’a yi wa yankin sakiyar da ba ruwa ba.

Shugaban gamayyar kungiyoyin Jamilu Aliyu Charanci ya ce arewa ka iya samun dimbin kudin shiga daga albarkatun noma da kiwo matukar aka tabbatar ana karbar haraji kan duk buhun abinci da za’a fitar daga arewa a kuma daina kai shanu kai tsaye kudu maimakon haka a rika yankawa a na tura naman.

Wannan matsaya ta zo dai-dai da hangen tsohon sakataren gwamnati Mista Babachir David Lawan, wanda ya yi misali da arzikin noma da kiwo na jihar Adamawa “an tare ka an kirga shanu a ka ce kowace saniya ka biya haraji Naira dubu biyar, na yi lissafi a shekara ba za mu gaza samun akalla Naira Bilyan kusan dari ba. A na zuwa Mubi a na siyan shanu 300,000-400,000 to in ka kara N5000 a kai ya yi wani abu ne?”

A karshe Jamilu Charanci ya yi hannunka mai sanda ga ‘yan majalisar “al’umma su tashi su rike ‘yan majalisar su gam, wannan kudurin idan ya tsallake ba wadanda su ka cuce mu sai ‘yan majalisar mu, idan kuma a ka maido shi a ka janye shi to ku sani ba wanda ya taimake mu sai ‘yan majalisar mu”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp