Home General Arewa Na Da Hanyoyin Tara Haraji Daga VAT Da Dama – CNG

Arewa Na Da Hanyoyin Tara Haraji Daga VAT Da Dama – CNG

Gamayyar kungiyoyin arewacin Najeriya CNG, ta ce yankin arewa na da dimbin hanyoyin tara harajin da za su cike gurbin kudurin dokar sabunta haraji da ke gaban majalisar dattawa.

Wannan ya biyo bayan zama da kwararru kan hanyoyin raya tattalin arziki, da kungiyar ta yi a Abuja don neman mafita idan kudurin ya samu nasara.

CNG wacce ta sake nanata bukatar dakatar da kudurin don yi ma sa garambawul da zai dace da muradun kowane yanki, ta ce hakkin ya rataya a kan ‘yan Arewa a majalisa su tabbatar ba’a yi wa yankin sakiyar da ba ruwa ba.

Shugaban gamayyar kungiyoyin Jamilu Aliyu Charanci ya ce arewa ka iya samun dimbin kudin shiga daga albarkatun noma da kiwo matukar aka tabbatar ana karbar haraji kan duk buhun abinci da za’a fitar daga arewa a kuma daina kai shanu kai tsaye kudu maimakon haka a rika yankawa a na tura naman.

Wannan matsaya ta zo dai-dai da hangen tsohon sakataren gwamnati Mista Babachir David Lawan, wanda ya yi misali da arzikin noma da kiwo na jihar Adamawa “an tare ka an kirga shanu a ka ce kowace saniya ka biya haraji Naira dubu biyar, na yi lissafi a shekara ba za mu gaza samun akalla Naira Bilyan kusan dari ba. A na zuwa Mubi a na siyan shanu 300,000-400,000 to in ka kara N5000 a kai ya yi wani abu ne?”

A karshe Jamilu Charanci ya yi hannunka mai sanda ga ‘yan majalisar “al’umma su tashi su rike ‘yan majalisar su gam, wannan kudurin idan ya tsallake ba wadanda su ka cuce mu sai ‘yan majalisar mu, idan kuma a ka maido shi a ka janye shi to ku sani ba wanda ya taimake mu sai ‘yan majalisar mu”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp