Hukumar Kula da Zirga- zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta musanta jita-jitar da ake yadawa na fara daukar aiki a Hukumar.
Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a ranar lahadi, ta bakin mai magana da yawun Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa inda Yace Babu gaskiya a batun daukar Sabbin Ma’aikata.
Nabilusi Kofar Na’isa Ya ce Hukumar ta lura da jita-jitar da ake yadawa na fara daukar sabbin Jami’an Hukumar wadanda hakan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.
Read Also:
Sai dai Kuma sanarwar tace Hukumar na tsaka da aikin tantance daukacin Jami’an KAROTA domin duba yuiwuwar daukar sabbi.
A don haka Hukumar ke gargadin jama’a, da su guji yada jita-jitar fara daukar sabbin Jami’an na Hukumar ta KAROTA
Hukumar ta ce duk wanda ta kama da hannu wajen yada jita-jitar zata dauki matakin sharia a kansa.
Engr. Faisal ya roki jama’a da su yi gaggawar sanar da Hukumar ta KAROTA ko ofishin ‘Yansanda mafi kusa wanda duk aka samu yana yada jita-jitar
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1487 days 19 hours 16 minutes 25 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1469 days 20 hours 57 minutes 50 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com