Kotun ta yankewa mutum biyar hukuncin kisa a Kano

Wata babbar kotu da ke Kano a Najeriya ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar ratay bayan kama su da laifin kisan wata tsohuwa bisa zargin maita.

Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin yin silar mutuwar tsohuwar mai shekara 67 a duniya a ranar 15 ga watan Nuwamban 2023, ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba.

A lokacin yanke hukuncin, mai shari’a Usman Na’abba ya bayyana cewa kotun ta samu hujjoji ƙarara da suka tabbatar da laifin waɗanda ake tuhuma.

Lamarin dai ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke ƙaramar hukumar Wudil ta jihar Kano.

Maita da tsafi abubuwa ne da ke yawan janyo cece-ku-ce a ƙasashen Afirka, inda iyalai kan ɗauki mataki kan mutanen da suke zarga da sanadin kashe musamman yara ta hanyar maita.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 12 hours 1 minute 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 13 hours 42 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com