Dangote ya sake rage farashin Man fetur

Matatar mai ta Dangote ta bayyana cewa ta rage farashin man daga Naira N890 zuwa Naira N825 duk lita

Wannan na cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar inda ya ce ya rage farashin man ne sakamakon karatowar watan azumin Ramadan, don tallafawa yunkurin shugaban kasa na sasauta al’amura a Nijeriya.

Wannan ne dai karo na biyu a watan fabarairu da Dangote ya rage farashin man fetur bayan karin da aka samu kwanakin baya.

Sanarwar ta ce Sabon farashin zai fara aiki ne daga ranar 27th February 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com