Home General Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban Namibia

Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban Namibia

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon shugaban ƙasar Namibia, Dr. Sam Nujoma.

Tinubu wanda mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta a wajen jana’izar ban girman da aka yi wa marigarin ya bayyana shi a matsayin jarumin da ya ƙarfafa wa ƙasashen Afirka gwiwa wajen neman ƴancin kansu.

Yayin da yake jawabi a wajen jana’izar, Kashim Shettima ya ce ƙasashen Afirka ba za su manta irin gudunmawar da Mista Nujoma ya ba su wajen tabbatar da ƴancin kawunansu ba.

Najoma wanda shi ne shugaban Namibia na farko – ya rasu ne a ranar 8 ga watan Fabrairu, yana da shekara 95 a duniya, bayan fama da jinya a wani asibiti a Windhoek, babban birnin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp